Connect with us

HARKAR TSARO

Bikin Nadin Sarkin Dawan Matasa Ya Haddasa Rigima A Maraba

Published

on

Bukin kaddamar da Sarkin Dawan matasa na anguwar Maraba a jihar Nassarawa ya haddasa yamutsi inda wasu su ka dauka fitina ce ta tashi.

Rahotanni sun baiyana cewa matasa masu dawa sun fito da makamai gefen titi su na wasa da hakan ya jawo razanar wasu su ka dauki hari a ka kawo mu su.

Musamman mutanen kudancin Najeriya da ba su san yanayin masu dawa ba, sun firgita ainun inda har lamarin ya kai makwabciyar anguwar Masaka.

Yanzu dai duk lamura sun daidaita bayan fahimtar cewa ba wani sabon tashin hankali ba ne.

HARKAR TSARO

Kotun koli ta baiwa Amerkawa damar riƙe bindiga dan kare kai

Published

on

By

Kotun koli a Amirka ta zartas da hukuncin bai wa jama’a izinin yawo da bindiga don kare kai a sabanin kiran da aka yi na tsaurara dokokin mallakar bindiga.
Kotun Koli a Amirka ta zartas da hukuncin bai wa jama’a da shekarunsu na mallakar bindiga ya kai, izinin yawo da bindiga don kare kansu sabanin kiraye-kirayen neman an takaita hakkin mallakar bindiga a kasar.

Ma’aikatar da ke kula da ‘yancin masu mallakar makamai ta yaba da hukuncin da ya kawo karshen dambarwar da ta barke kan takaita hakkin mallakar makamai a baya-bayan nan a cikin kasar. Kawo yanzu ana da akalla bindigogi miliyan casa’in da ke yawo a hannun Amirkawa. Tuni Shugaba Joe Biden ya baiyana takaici kan hukuncin kotun.

Dambarwar ta barke a baya-bayan nan a kasar kan takaita amfani da bindiga a sakamakon yawan harbin kan mai uwa da wabi da suka yi sanadiyar salwantar rayuka a sassan kasar. Rahotanni sun gano cewa, an fi samun asarar rayuka ta hanyar amfani da bindigogi a Amirka fiye da rayukan da ke salwanta a tsakanin sojojin kasar da ke a fagen daga koma hatsarin mota da sauran iftala’i.

Continue Reading

HARKAR TSARO

Yadda Al’umar Ibbi suka yi nasara kan masu garkuwa da mutane

Published

on

Daga Lado Salisu Muhammad Garba 

Alumma mazauna yankin sarkin kudu
dake karamar hukumar Ibbi a jihar Taraba, sunyi fito na fito da masu garkuwa da mutane har suka kashe biyu daga chikin masu garkuwan.

Wani mazaunin yankin da abin ya faru da ya bukachi a sakaye sunansa, ya bayyana mana cewa, “masu garkuwan sun bukachi da wani daya basu kudi naira dubu dari shida domin su saka katin Waya, don su rinka kiranshi kafinsu zo karbar miliyan biyar amatsayin kudin fansa, su kuwa mazauna yakin suka hada Kai suka kuwa yi musu Kofar rago har su kayi nasarar kashe yan garkuwan biyu a wannan fito na fiton, a wannan yankin.

Rundunar ‘Yan sandan jihar Taraba sun tabbatar da aukuwar lamarin ta bakin mai magana da Nyawun rondunar yan sandan jihar DSP, Usman Abdullahi, gawarwakin masu garkuwan da hukumar yansadan suka je daukowa ma har sun fara lalachiwa.

Alhaji Alhassan Hamman Gassol kwamishinan riko na ma’aikar yada labarai a jihar Taraba, wanda yace gwamnatin jihar ta ma fara tataunawa da masarautun gargajiya na jihar musamman kananan hukumominda lamarin yayi kamari a jihar Taraban gabadaya domin ganin an shawo kan mastalar rashin staron da ya addabi jihar.

Continue Reading

HARKAR TSARO

TARO KARO NA 17 MAI TAKEN MASU TA’ANNATI DA KAFAFEN YAƊA LABARAI NA ZAMI MAI ALAƘA DA FARAR HULA DA SOJI

Published

on

TARO KARO NA 17 MAI TAKEN MASU TA’ANNATI DA KAFAFEN YAƊA LABARAI NA ZAMI MAI ALAƘA DA FARAR HULA DA SOJI

 

Taron ƙarawa juna sani na kwana ɗaya da haɗin gwiwar Rundunar Sojoji ta ƙasa ɓangaren masu hulɗa da farar Hula, tareda ƙungiyar Security Affairs Limited, wanda aka gudanar a ranar Laraba 25/01/22 a Otal din City Green dake ƴola jahar Adamawa.

Jigon Taron shine: Imperatives of Non-kinetic line of Operations in Asymmetric Warfare, wand babban hafsan soji mai hulɗa da jama’a na sojan Najeriya Manjo Janar MG Kangye ne ya jagoranci taron ƙarawa juna sanin.

A cikin jawabinsa, Kangye ya jaddada bukatar samar da kyakykyawan alaƙa tsakanin farar hula da Sojoji wajen tunkarar makiyinmu ɗaya, wato rashin tsaro.

A yayin ƙaddamar da takarda ta ɗaya wanda Maj. Gen. Eap. Undiandeye, psc plsc fdc ICTF DSS MASSS Msc fcm Fcai, Director Psychological Warfare Defense Headquarters, ya ƙaddamar ya nuna bukatar ƴan Jaridu, ƙugiyoyin siyasa da sauran masu ta’ammali da kafafen yaɗa labarai na zamani (social media) su kasance masu tantance labari dakuma sanin sahihacin labari kafin yaɗawa.

Sannan ya nuna irin illa da ka iya faruwa idan har aka yi amfani da kafofin ba bisa yadda ya dace ba, yace “ko wannan zanga-zangar ta neman kawar da rundunar SARS wadda ta jawo babbar naƙaso ga Najeriya ma ta (Social Media) aka somata, sabida haka mu zamo masu haƙuri da amfani da kafafen yadda ya kamata cikin ili.”

Mai gabatar da takarda na biyu Dokta Lanre Adebayo ya bayyana irin rawar da kafafen sadarwar zamani ke takawa, wadda suka haɗa da samar da zaman lafiya da kuma kare martabar Najeriya ta hanyar baiwa Jami’an tsaro sahihan bayanan da ake buƙata, musamman na Sojoji.

Yakuma ce “Sojoji da ƴan Jaridu su kasance masu haƙuri da juna domin samar da mafita ga ƙasar, sabida abinda ka shuka shi zaka girɓa.”

Taron ya samu halartar Masu Ta’ammali da kafafen yaɗa labarai na zamani (Social Media) da ƴan Jaridu da Sarakunan Gargajiya da Ƙungiyoyin fararen hula dadai sauransu.

Kanwa uwar gami wanda shine Ummul’abaisa na gudanar taron, Amb. Austin Peacemaker shugaban ƙungiyar  Security Affairs Limited,  shi ya kasance mutum na ƙarshe da yayi jawabi, inda ya godewa mahalarta taron da nuna buƙatar al’umma su zamu masu kishin ƙasa.

A ƙarshe, an karrama mahalarta taron da takardar shaidar halarta, da wata ihsani domin rakiya.

Continue Reading

BABBAN LABARI

Copyright © 2020 VOA voiceofarewa.ng