Connect with us

BINDIDDIGI

Dagaske ne Salihu Tanko Yakasai ya bar Najeriya kamar yadda aka wallafa a baya?

Published

on

Tun bayan ficewa daga Nigeria zuwa hutu a ƙasar Amurka da Salihu Tanko Yakasai yayi, wasu kalamai mabanbanta na ta fitowa akan wannan Tsoho hadimin Gwamnan jihar Kano Dr Abdullahi Umar Gandauje

Kalaman da ke nuni da cewa ya ƙaura a Najeriya Wanda wasu daga ciki jaridu na Shafukan sada zumunta, suka wallafa labarin

Saidai Salihu Tanko Yakasai ya musan ta wannan proparganda da akayi ta haɗawa wanda yanzu haka ma ya wallafa labarin kammala hutunsa a ƙasar Amurka, kuma tuni yana kan hanyar zuwa gida wato Kano a Najeriya


Salisu Tanko Yakasai da wallafa hakan bayan awa ɗaya daya wuce a shafinsa na facebook yana cewa

“Alhamdulilah na kammala hutu na a kasar America kuma ina kan hanya ta ta komawa Kano tumbin giwa, ko da mey ka zo mun fi ka, duk dadin turai bata kai gida kwanciyar hankali ba. Ka sakata ka wala sai a gida, ka ci gurasa da masa, ka ci tuwo da man shanu, ka sha koko da kosai. Ka ji kiran sallah ta ko ina, ka ga yan’uwa da abokan arziki. Fatan mu shi ne, Allah sa Kano da arewa da Najeriya ta samu ci gaba da duk wani abun da yake ba mu shaawa a turai, da sauran kasashen da suka ci gaba, muma mu same shi a nan. Da yardar Allah, wannan lokaci zai zo, ko ba’a zamanin mu ba, toh a zamanin ‘ya’yan mu da jikokin mu in sha Allah. Amin Ya Rahman. 👏

Salihu Tanko Yakasai (Dawisu)
Masoyin Kano da Arewa da Najeriya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

BINDIDDIGI

Mutane miliyan 7 na bukatar taimakon jin kai a arewa maso-gabashin Najeriya

Published

on

By

 

Sakamakon ta’addancin kungiyar Boko Haram, mutane miliyan 7 ne ke bukatar taimakon jin kai a arewa maso-gabashin Najeriya.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito Mai Bawa Shugaban Kasa Shawara Kan Sha’anin Tsaro Babagana Monguno na jawabi a wajen Karo na Biyu na Taron Hukumomin Yaki Ta’addanci a Kasashe Mambobin Majalisar Dinkin Duniya da aka gudanar.

A jawabin nasa, Monguno ya shaida cewa, ta’addanci na ci gaba da yin barazana ga duniya ba tare da nuna bambancin kasa, launin fata, yare ko addini ba.

Monguno ya kara da cewa, ta’addanci a lokacin hadewar duniya waje guda ya zama wani babban makami da ake amfani da shi ga wasu mutane, kuma a yanzu akwai mutane miliyan 7 da ke bukatar taimakon jin kai a arewa maso-gabashin Najeriya.

Ya ce, “Baya da annoba, ibtila’o’i da sauyin yanayi, ta’addanci ne babban makiyin dan adam da ke yi masa barazanar wanzuwa.”

Rahotun TRT

Continue Reading

BINDIDDIGI

Tasirin Social Media A Wurin Yara Masu Tasowa: Shawara Ga Iyaye

Published

on

 

Tun da hukumar jarrabawa ta Jamb ta fitar da sakamakon jarrabawa labari ya chanja. Mafi yawa daga cikin yara sun fadi. Gaskiyar magana shine yaran yanzu ko kadan hankalin su baya kan karatu, da dama daga cikin su. Wannan kuma yana faruwa ne sakamakon shigowan kafafen sadarwa na zamani irin su Tiktok, Snapchat, Instagram da dai makamantan su.

Wadannan kafafen sadarwa ba komai suke yi ba illa kara rudar da yaran mu da kannen mu. Ka dauki Tiktok Misali; App ne da yake bada dama ga yaro ko yarinya su dinga tikar rawa suna recording din kan su yanda suke so. Idan ka bude Tiktok yanzu zaka ga yarinya da himar tana kwasar rawa, kaga namiji ya zage yana kwaiwayar muryar mace kaman dan daudu, ko ya dinga rawa, kaga yarinya tana rawa a cikin gidan su na mutunci alhalin wakan da take rawar sa bata ma san me ake fada ba, sannan ta bude shi ta aika zuwa ga duniya kowa ya gani yace ta iya.

Snapchat da Instagram duka kafafe ne da yanzu yara ke amfani dashi wajen gasa na karya, da nuna abun hannu ko da kuwa gidan su babu. Da dama yanzu zaka samu yarinya akan ta samu followers a instagram ba kalar ashararanci da ba zata yi ba. Zata bankare bayan ta, ta turo kirjin ta, ta yi duk wani salo na nuna tsarin jikin ta don ta samu followers. Idan kuma ta samu wadannan followers, abu na gaba shine ta cigaba da yi musu hotuna don su gani su yaba kyan ta ko surar jikin ta.

Muna cikin lokaci mafi hatsari, wadannan kafafen sadarwa yanzu sune a kwakwalwar yaran mu da kanne mu. Karatu ko kadan baya gaban da yawa daga cikin su illa kalilan wadanda Allah ya tseratar.

Saboda haka iyaye ku tashi tsaye, ku san me yaran ku suke yi da wayoyin da kuke saya musu don suyi karatu. Kada ku bari social media ya halaka yaran ku alhalin kuna da ikon hanawa.

Mahmud Isa Yola

Continue Reading

BINDIDDIGI

Wannan ita ce Addu’ar da tsohon hadimin Gwamnan jahar Kano Hon. Salihu Tanko Yakasai yayi a safiyar Jumma’a, Allah ka’amsamana

Published

on

 

Wannan ita ce Addu’ar tsohon hadimin Gwamnan jahar Kano Hon. Salihu Tanko Yakasai, yayi a safiyar Jumma’a Allah ka’amsamana.

Ya wallafa a shafin sa na sada zumunta na facebook

 

Alhamdulilah Ya Allah! Ya Allah Ka kara mana kaifin basira, Ya Rabbi Ka kara mana ilimi mai amfani kuma Ka ba mu ikon aiki da shi. Ya Raheem Ka dauwamar da mu a tafarkin Ka, Ya Allah Ka haskaka mana hanyar mu, Ka sharey mana duk wata matsala a rayuwar mu, Ka warware mana duk wani abinda yake addabar mu, Ka kare mu daga sharrin ma su sharri, Ka tsarkake mana zuciyar mu da tunanin mu. Alfarmar Annabi Muhammadu SAW, da Alqurani Mai Girma. Amin Ya Rabbi. Barka da jumaah yan’uwa Musulmi.

Salihu Tanko Yakasai (Dawisu)
Masoyin Kano da Arewa da Najeriya.

Continue Reading

BABBAN LABARI

Copyright © 2020 VOA voiceofarewa.ng