Connect with us

NISHADI

Hotunan Jaruma Nafisat Abdullahi na karshen mako don masoyanta

Published

on

Jaruma Nafisat Abdullahi, ta sako kyawawan hotunanta na karshen mako ga masoyanta.

 

 

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

NISHADI

Maganar Ladin Sima gaskiya ne – Naziru Sarkin Waƙa

Published

on

Maganar Ladin Sima gaskiya ne – Naziru Sarkin Waƙa

Naziru serkin waƙa, ya gaskata Ladin Sima, a kan batun rashin biyan masu fitowa a film yadda ya kamata.

Sarkin Waƙa ya ƙalubanci su Falalu da Ali Nuhi da su fito suyi rantsuwar ƙaryata batun idan ƙarya aka musu, inji shi.

Bayanan hakan ya sako su ne a shafinsa na facebook cikin Bidiyo mai tsawon mini 6 da daƙiƙu 45.

Tirka-tirkan ya samo asali ne bayan hira da BBC Hausa ta yi da Ladin Sima a cikin shirinta na Daga Bakin Mai Ita, inda ta bayyana cewa a duk finafinai da ta fita ba’a taɓa biyanta naira dubu 40 ko 50 ba, hasali ma tace a ranar da suka gudanar da tattaunawar ma ta je ɗaukar Film naira dubu 2 aka biyata.

Continue Reading

NISHADI

Ranar Bikin Farar Kaza su Balbela ba sai angayyace suba. Hajiya Zainab Abdurrahman Mai Agogo

Published

on

A madadin ɗaukacin ma’aikatan kamfanin Binkola Communication Services, da Shafin Voice of Arewa VOA, muna  taya shugabar  kamfanin ta WhiteBlood Multimedia Services, kamfanin da ke da mallakin shafin Kakaki Hausa da Farin Jini TV, Hajiya Zainab Abdurrahman Mai Agogo murnar zagayowar ranar haihuwarta a wannan rana ta 8 ga watan Yunin shekarar 2021.

Zainab Abdurrahman Mai Agogo fitacciyar yar jarida ce a jihar Kano da ta yi aiki a gidajen rediyo daban – daban da ke Kano, kuma tana cikin mata ƙalilan da su ka samu gogewa dai-dai da zamani a harkar yaɗa labarai, wanda hakan ne ya ba ta karfin gwiwar buɗe kamfanin WhiteBlood Multimedia Services.

Haƙiƙa Zainab Abdurrahman Mai Agogo tana daga cikin ƴan jarida mata a jihar Kano da ma arewacin Najeriya da su ka karɓi chanji a harkokin yaɗa labarai tare da komawa duniyar Intanet wajen yaɗa labarai da sauran shirye-shirye

A bisa haka muna addu’ar Allah ya sanya albarka a shekarun da suka gabata, da kuma Shekarun da za ki yi a nan gaba.

Continue Reading

NISHADI

Ranar Waƙa Ta Duniya: Wani Mawaƙi Ne a ranku?

Published

on

Daga Kakaki Hausa.

Ranar 21 ga watan Maris ɗin kowacce shekara rana ce da Majalisar dinkin Duniya ta ware domin jaddada muihimmancin rubutacciyar waka ga al’ummar duniya gaba daya dangane da ilimantarwa da fadakarwa da kuma samar da nishadi.

Rubutacciyar wakar, kamar yadda majalisar ta ce, hanya ce da ke bayyana halayen al’umma da al’adunsu da fasaharsu. Haka kuma wani tsari ne na samar da kaifafa tunani da natsuwar ruhin dan Adam, don haka ne ma majalisar ta ware rana ta musamman domin tunawa da ita.

An tabbatar da ranar 21 ga Maris ce a matsayin ranar Bikin Rubutattun Wakoki ta Duniya a yayin taron kungiyar Bunkasa Ilimi ta Majalisar dinkin Duniya (UNESCO), karo na 30 da ya gudana a birnin Paris, kasar Faransa, a shekarar 1999.

Continue Reading

BABBAN LABARI

Copyright © 2020 VOA voiceofarewa.ng