Connect with us

DAGA JIHOHI

Shirin Bada Tallafi: Matasan Adamawa Zasu dara- Inji Hon. Iliya James

Published

on

Daga Abubakar Halidu

Yanzu haka a wani sabon yunkuri na samarwa matasa  ayyukan yi da kuma dogaro da kai, gwamnatin jihar Adamawa ta  buɗe shafin tattara bayanai na matasa masu fasaha, ciki harda ƙungiyoyin mata masu sana’o’i domin tallafa musu da jari.

Wannan sabon shiri dai na  karkashin ma’aikatar samar da ayyukanyi  da cigaba na jahar Adamawa, kuma tuni har an a buɗe shafin domin matasa maza da mata waɗanda basa aikin gwamnati su cika bayanan su.

Shafin dai an buɗe shi a watan mayu 2020, wanda ya yi makonni, inda aka ɗauki bayanan waɗanda suka gama makaranta kama daga sakandare, makarantar gaba da sakandare, da ma Jami’a, har da ma masu basira da basu gama makaranta ba, da masu buƙata ta musamman.

Da yake jawabi yayin taron ganawa da kungiyoyi, Kwamishinan ma’aikatar samar da ayyukanyi  da cigaba na jahar Adamawa,  Hon. Iliya James, ya ce, “shafin an buɗe ne ga masu shekaru 18 zuwa 45 a jahar.

“Wanna dai gwamnati ta kawo shi ne, don koyar wa matasa sana’o’i daban-daban a makarantu da ake koyar da sana’o’i da sauran wasu wurare,” a cewar sa.

James ya bayyana cewa taron an yi shi ne da nufin ganawa da jami’an  na hukumomin raya ƙananan ƴan kasuwa da masana’antu na tarayya (SMEDAN) da ta Jaha, domin ƙarin haske akan shirin tallafin.

A don haka ne kwamishinan  ya ƙirayi matasa da su yi ƙokarin cika bayanan su a wani shiri na tallafawa matasa na National Youth Investment Funds wanda aka buɗe ranar 14/10/2020 don samun shiga tsarin tallafi na kuɗi daga gwamnati.

Yayin da yake jawabi akan wanda zai iya cin gajiyar tsarin tallafawa ƙananan ƴan kasuwa da masu ƙananan masana’antu SME’s, Mustapha Ali-Gana ya ce.

“Duk wata ƙungiya ta ƴan kasuwa da take da rijista da corporate Affairs Commission (CAC) da kuma SMEDAN to tana da damar cin gajiyar wanna tasiri na tallafin amman banda ƙungiyoyi na shafukan sada zumunta.”

“Sannan babu wata rijista da ake gudanarwa a kan teburi  da sunan  SME’s ko SMEDAN a halin yanzu, duk a kan yanar gizo ake yi,”

Mustapha ya kara da cewa,  “mutane su gane cewa takardan shaida da suke da shi na SMEDAN, akwai lambobi na musamman akan takardar da aka turawa kowa bayan ya cika, da ita zaku yi amfani wajen cika tsarin Survival Funds wadda ake cikawa a halin yanzu.”

7 Comments

7 Comments

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

DAGA JIHOHI

ƘUNGIYAR AYCMF TA GUDANAR DA TARUKA A JIHOHI SHIDA 22/5/2022

Published

on

KUNGIYAR MATASAN AREWACIN NIGERIA “AREWA YOUTHS CONCERN MEDIA FORUM” (AYCMF) TA GUDANAR DA TARUKA A JIHOHI SHIDA 22/5/2022.

 

Daga Kungiyar: Matasan Arewacin Nigeria “Arewa Youths Concern Media Forum” (AYCMF)

 

Tarukan sun gudana a jihohin Bauchi Borno Kaduna Gombe Kano Sokoto. anyi taron ne domin wayar wa yan uwa matasa kai dangane da halin da Arewa da al’ummar Arewa suke ciki da kokarin nunawa matasan mu muhimmancin hadin kai domin magance wasu daga cikin matsalolin matasan na arewa.

 

Taron ya maida hankali wajen kokarin nunawa matasa muhimmancin hadin kai a tsakanin mu domin tunkarar matsalolin yankin mu da dukkan karfin mu mussamman abunda yake ci mana tuwo a kwarya wato ta’addanci. kungiyar AYCMF ta tattauna sosai akan hanyoyin da za abi a dakile tunanin ta’addanci a kwakwalen matasan mu masu tasowa.

 

Kungiyar AYCMF tana fafutukar hada kan matasan Arewa a jihohi 19 da Abuja 20 domin mu zama tsintsiya madaurinki daya. masu magana da murya daya. karkashin inuwar Kungiyar domin cimma kyawawan manufofin ta guda biyar (5) da take aiki akai.

 

Kungiyar AYCMF tana maraba da dukkan wani matashi Namiji ko Mace mai kishin Arewa da al’ummar Arewa. kuzo mu hada kai domin samar da cigaban matasan mu a cikin kasar mu Nigeria. ayyukan kungiyar AYCMF yana fantsama lungu da sakon Arewacin Nigeria muna bukatar karin dakaru domin tabbatar da kyawawan manufofin kungiyar.

 

Kofar wannan kungiya abude take ga dukkan wani matashi mai kishin Arewa da al’ummar Arewa. kuzo mu hada kai domin dawo da martabar yankin mu da al’ummar mu a idon duniya.

 

Allah ya zaunar da Arewa lfy ya hada kawunan mu. mu zama tsintsiya madaurinki daya.

Sign:

AYCMF MANAGEMENT

22/5/2022

Continue Reading

DAGA JIHOHI

EFCC Na Zargin Tsohon Gwamnan Kano

Published

on

Daga Mujahid Wada Musa Kano

hukumar da ta ke yaki da hana cin hanci da rashawa EFCC ta garkame wani kango da kuma asibitin da ke jikinsa a unguwar Bompai ,mallakin tsohon gwamnan jahar Dr. Rabiu Musa Kwankwaso.

Tsohon gwamnan yana fuskantar zargi ne daga wasu ƴan fansho inda suka shigar da kararsa a shekarar 2015.
Asibitin da hukumar ta EFCC ta garkame din shi ne wanda ya bawa gwamnatin jahar Kano a lokacin da cutar corona ta fara kamari akasarnan dan killace masu fama da ita amma gwamnatin Kanon bata karba ba.

Sai dai wasu rahotanni mai kwanan watan 27 ga watan mayu na 2015 kwankwaso ya karbi gudunmawar naira miliyan 70-saba’in daga kananan hukumomi 44 na jahar Kano da jumullar kudi ya kai sama da biliyan 3 dan yakin neman zabensa na takarar shugaban kasa a 2015.

Continue Reading

DAGA JIHOHI

Ƴan bindiga sun hallaka ‘sama da mutum 35’ a jahar Zamfara

Published

on

By

Rahotanni daga jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun kashe sama da mutum 40 a jerin hare-hare da suka kai a wasu kauyukan jihar.

Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da kai harin, amma ta shaida wa BBC Hausa cewa mutum 35 aka kashe.

Lamarin ya faru ne a ƙauyuka fiye da biyar da ke karamar hukumar Maradun da ranar Alhamis sai dai bayanai ba su fito ba sai Juma’a.

Ganau sun shaida wa BBC cewa maharan sun je ƙauyukan Gidan Adamu da Gidan Maidaji da Bauci da Wari da Kyara da Gidan Maidawa kan babura sannan suka buɗe wuta.

Lamarin ya yi sanadin mutuwar mutum 42, a cewar wani mutum da muka tattauna da shi.

“Wannan lamari ya faru ne a jiya Alhamis tun daga karfe 12 na rana har zuwa bayan la’asar, a lokacin da ‘yan bindigar suka shiga shiyyar kan babura sama da 100,” in ji wani da ya shaida lamarin.

Wannan hari na zuwa ne kwana biyu kacal bayan da ƴn bindiga suka kashe mutum 18 a jihar Katsina.

Sannan kuma waɗannan hare-hare duk sun faru ne a yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da ƙoƙarin cetofiye da ɗalibai 100 da aka sace a wata makarantar kwana a jihar Kaduna.

Satar ɗaliban ita ce ta baya-baya cikin lamari irin sa da yake neman zama ruwan dare a arewacin Najeriya.

Continue Reading

BABBAN LABARI

Copyright © 2020 VOA voiceofarewa.ng