Connect with us

BABBAN LABARI

Sojoji da CJTF sun ceto wasu manoma daga hannun yan Boko Haram a jihar Borno

Published

on

 

Rahotanni dake shigowa yanzu na cewa sojojin kundunbala da mayakan Civilian JTF sun kubutar da mutanen kauyen Zabarmari manoman shinkafa a kalla 200 daga ‘yan ta’addan Boko Haram

 

Idan ba’a manta ba, ranar lahadi da ta gabata ne ‘yan ta’addan Boko Haram suka yiwa mutanen Zabarmari 43 kisan gilla ta hanyar yankan rago, sannan suka tafi da daruruwan mutane jeji.

 

BABBAN LABARI

Matashin kansilan Hon. Aminu Sa’adu Mo-Allah-Yiɗi Ya Bada Umurnin Gina Magudanan Ruwa Cikin Gaggawa

Published

on

By

Jim kaɗan bayan kokawa kansilan Mazaɓar anguwa Lamorde dake ƙaramar hukumar Mubi ta Kudu a Jahar Adamawa
Hon Aminu Sa’adu Mo-Allah-Yidi. Kan matsalar rushewar wannan magunan ruwan

Hon. Aminu Ya dauki matakin gaggawa dan farantawa da kuma tsare rayuwan jama’ar wannan anguwa. na Lamorde

Hon. Aminu dai ya gina mugudan ruwan da manyan block wanda girmansu yakai inci tara, tare da yin anfani da kayan aiki masu ƙargo a cewar ma’aikatan daka gina wannan magudanan ruwan

Kansila Lamorde Ward, Hon Aminu yayi alƙawarin kammala wannan aikin cikin gaggawa ganin yadda aka fiskanci damuna, Mubi South dai na daya daga cikin yankunan da ake sa ran za’a iya sake zaben cike giɓi a wannan asabar

Hakan yasa Hon. Aminu Ya roki mazauna yankin da su taimaka su zaɓi Gwamna Fintiri dan cigaba samun wasu ayyuka a yankin dama jihar Adamawa baki ɗaya

Hon Aminu dai kansila ne dake anguwa Lamorde a Mubi South na Jahar Adamawa wanda ya ciki shekara ɗaya da zaman kansila a Lamorde

Matashin kansilan Hon. Aminu yayi alƙawarin sake baza ayyukan tare da samarwa matasa abin dogaro da kai matuƙar Gwamna Fintiri ya samu damar zarcewa a karo na biyu.

Continue Reading

BABBAN LABARI

Matashin da aka yi yunƙurin cire wa ƙoda domin bai wa ƴar Ekweremadu

Published

on

By

Kotu ta samu Sanata Ike Ikweremadu da matarsa Beatrice da laifin yunƙurin cire ƙodar wani saurayi talaka, ta hanyar kai shi London domin ya bayar da ƙodar.

BBC ta binciko yadda lamarin ya faru, yayin da suke jiran a yanke masu hukunci.

Sonia Ekweremadu, wadda ɗaliba a ɗaya daga cikin jami’o’i mafiya shahara a Birtaniya, ta fito ne daga gidan masu hali, kuma ɗaya daga cikin manyan ƴan siyasa a Najeriya,

To amma tana fama da rashin lafiya, kuma tana matuƙar buƙatar wanda zai ba ta ƙoda.

Mahaifinta, Ekweremadu ya biya dillalai dubban kuɗaɗen Birtaniya domin samo wanda zai bayar da gudummawar ƙodar.

Daniel, wanda ba za mu bayyana sunansa ba, ya taso ne a wani iyali mai girma da ke rayuwa a wani ƙauye a Najeriya, inda babu ruwan famfo kuma babu lantarki.

Yana da shekara 15, kuma yana sana’ar sayar da kayan wayar hannu a cikin baro, a birnin Legas, inda yake tura wa iyayensa ɗan abin da ya samu.

A 2022, lokacin yana da shekara 21, ya shiga wani ofishin ƴan sanda da ke kusa da Heathrow, a gajiye, cikin tashin hankali.

Ya shaida wa ƴan sanda cewar ya tsere ne bayan da wasu mutane suka yi yunƙurin cire ɗaya daga cikin ƙodarsa.

A ɗaya ɓangaren kuwa, yayin da Daniel ke tura baro, Ike Ikweremadu da matarsa Beatrice na cikin tashin hankali kan rashin lafiyar ƴarsu Beatrice, wadda za ta iya rasa ranta.

Iyalin Ikweremadu sun tunkari wani mutum mai suna Dr Obinna Obeta, wanda shi ma ya samu gudumawar ƙoda a 2021, wanda aka yi masa aiki a asibitin Royal Cambridge Hospital.

Ike Ekweremadu

Iyalan Ikweremadu sun so ne Dr Obeta ya sake kwatanta abin da ya faru da shi a kan ƴarsu Sonia

Daga nan ne Dr Obeta ya buƙaci wanda ya ba shi gudumawar tasa kodar da ya binciko wanda zai bai wa Sonia gudummawar tasa ƙodar.

Inda aka bayar da sunan Daniel.

Daniel ya bayyana cewa Dr Obeta ya yi alkawarin kai shi Landan amma bai faɗa masa cewar za a cire masa ƙoda ba.

Daniel ya ce wa kotu “Na zaci cewa zan zauna gidansa ne kuma zai nema min aiki. Ya ce min kada na faɗa wa kowa cewa zan je Birtaniya.”

Daniel ya zaci a kan batun takardar shiga Birtaniya ne, lokacin da Dr Obeta ya ce masa zai yi gwaje-gwaje a asibiti.

An ba Daniel takardar shiga Birtnayi ne a watan Janairun 2022.

Daniel ya ce na zaci taimakona zai yi.

Sai dai ya ce a lokacin da suka isa Landan ya zama tamkar ɗan aiki a gidan Dr Obeta.

Ta bayan fage kuwa Ike Ekweremadu na samun bayani daga wani ɗan uwansa, wanda shi ma likita ne, wanda aka umurce shi ya biya Dr Obeta kuɗi kimanin fan 2,000.

Shi kuwa Daniel an shirya cewa za a ba shi fan 6,000 kan ƙodar tasa, yayin da aikin musayar ƙodar za a yi shi a ɓangaren masu hannu da shuni na asibitin Royal Free da ke London kan kuɗi fan 80,000.

A Birtaniya laifi ne a biya wanda zai bayar da gudmawar wata gaɓa tashi, waɗanda yawanci ƴan uwa ne na kusa.

Da alama Ekweremadu da iyalansa sun san da wannan doka.

Sun gayyaci Daniel domin cin abinci a wani gidan cin abinci na mutanen Yammacin Afirka da ke London, kuma an buƙace shi ya sanya kaya masu kyau.

Sonia ma ta halarci wurin cin abincin har ma an ɗauki hotonta tare da Daniel.

Kotu ta wanke Sonia daga zargin hannu a cikin lamarin.

Sonia Ekweremadu tare da Daniel

A ranar 22 ga watan Fabarairun 2022 ne Daniel da Sonia da kuma babban likitan ƙoda Dr Peter Dupont suka haɗu a karon farko.

Daniel ya shaida wa kotu cewa: “Ya tambaye ni, cewa, ko na san cewar zan bayar da ƙodata. Na kaɗu. A ranar ne na fara jin wani abu wai shi dashen ƙoda.”

Ya ƙara da cewa a ranar ne ya fara jin sunan Ekweremadu: “Ina ta kuka, jikina na rawa.”

A wata takarda da ya rubuta yana neman shawara daga abokin aikinsa, Dr Dupont ya fadi cewa Daniel bai taɓa haɗuwa da Sonia, wadda aka yi iƙirarin cewa ƴar uwarsa ba ce sai a ranar.

Sannan likitan ya ce hankalinsa bai kwanta da maganar ba.

Wani likitan na biyu da aka kawo domin aikin, Dr Philip Masson, shi ma hankalinsa bai kwanta da lamarin ba kasancewar ya lura cewa Daniel bai fahimci haɗarin bayar da gudummawar ƙoda ba.

Daga nan ne Dr Dupont ya dakatar da batun dashen ƙodar, inda ya ce Daniel ba zai iya bayar da ƙodar ba kuma ba ya da alaƙa mai ƙarfi da wadda za a bai wa gudumawar ƙodar.

Sannan ba zai iya ɗaukar nauyin ci gaba da kula da lafiyarsa ba bayan aikin.

Sonia Ekweremadu na matuƙar buƙatar gudummawar ƙoda

A cikin makonni bayan haka, Ike Ikweremadu ya rinƙa tura wa Sonia hotunan waɗanda ake tunanin za su iya bayar da gudummawar ƙodar.

An ga yadda take ba shi amsa, tana cewa: “Wannan baƙin zai fi. Wannan farin da alama zai iya guduwa.”

A ɓangare ɗaya kuma wasu mutane biyu sun ziyarci Daniel a gidan Dr Obeta da ke kudancin birnin London.

Wani likita daga cikinsu ya danna cikin Daniel, abin da ya sanya hankalin Daniel ya tashi, ya yi tunanin cewa kila za su yi ƙoƙarin cire ƙodar ta hanyar tilasta masa da zarar ya koma Najeriya.

Daga nan ne ya garzaya wurin ƴansanda, inda aka samu nasarar kama Ekweremadu, da matarsa Beatrice da kuma ɗiyarsu Sonia, tare da Dr Obeta.

Yanzu an samu mutanen uku da laifin karya dokar hana bauta ta hanyar kai Daniel Birtanyia domin samar da ƙodar da za a sanya wa Sonia.

Continue Reading

BABBAN LABARI

Zaben Gwamnan Adamawa: Yadda Aishatu Dahiru Binani ke gab da kafa tarihi.

Published

on

By

*Meh yasa Fintiri yake kwaikwayon ayyukanta

*Hasashe ya bata kashi 70 na tazaran maki zuwaga nasara

*Yadda jin tsoronta ya ingiza Fintiri yake gudun wuce sa’a da kuma sayan kuri’u a fakaice

*Ainihin dalilan da suka sa Binani ke morewa daga samun goyon bayan mabiyanta

Daga: DAHIRU SANI

Sanata Aishatu Dahiru Ahmed Binani ta gama kintsawa tsab domin shiga gidan gomnati dake Dougirei a matsayin farkon zababbiyar gomna mace a Nigeria a ranar 18 ga watan Maris din 2023 a jahar Adamawa da akewa lakabi da kasar kyawawa.

Duba da yanayin jihan a yanzu kai tsaye mutum zai iya cewa saura yan kwanaki ne kafin Binani ta shiga gidan gomnati a matsayinta na wacce zata gaji gomna Ahmadu Umaru Fintiri muddin sahihan kuri’u ne ke kai mutum ga nasara.

Banda tsohon gomna Murtala Nyako babu wani dan takaran gomna daya samu gagarumin goyon bayan al’uma irin wadda Binani ta samu wadda hakan yasa da dama daga cikin jama’a sunyi imanin cewa a sauwake Binani zata shiga cikin gidan gomnati dake Dougirei.

Cibiyar bincike mai zaman kanta ta Democracy Watch Network (DWN) ita ce ta baiyana irin karbuwarta a wani gagarumin aikin jin ra’ayoyin jama’a data gudanar a jahan nan.

A cewar Mr. Stephen Godwin shugaban bincike da tsare-tsare na DWN Binani zatayi nasara ne da kaso 70 wadda hakan zai bata daman kafa tarihi a Jahan.

Yace ra’ayoyin a kalla mutum 500,000 akaji a tsakanin kananan hukumomi 21 tare da samun tabbacin kaso 95.

Yace matasa, mata da kuma masu larurar nakasa sune sukafi yin amanna da takaran tata duba da yadda kashi 80 daga ciki sukayi na’am da manufofinta suna mai tsammanin samun rayuwa mai inganci da samun kayakin tallafi wadda ya ceto iyalai da dama daga fadawa kangin talauci muddin Binani ta samu darewa kan kujeran iko a jahar Adamawa.

Yace ko shakka babu jajirtacciya kuma hazikan yar takaran na APC sanata Aishatu Binani mace mai kamar maza wacce tayi kaurin suna wurin tallafawa al’uma zata doke abokan karawarta musamman ma gomna mai ci a ko wani lokaci.

Tabbas sanata Binani zata girbe abunda ta shuka na gudanar da shugabanci mai nagarta da tallafawa jama’a inda aka ga ta karya lagon wadanda basu tabuka abun azo a gani idan suka sami dama.

Yadda kaddara da kiran jama’a ya ingiza Binani shiga siyasa

Ana alakanta shigan siyasan Binani akan kaddara da kuma kiran jama’a wadda wadannan abu biyun ne suka kaita ga wannan matakin duk kuwa da cewan hakan ya sabawa tunanin Dr. Ahmed Modibbo a tashin farko.

Kafin ta shiga siyasa, Binani ta kasance matashiyar yar kasuwa wacce ta sadaukar da dukiyanta akan jama’a. Saboda yadda take da burin taba rayuwar al’uma yasa ta bude wata gidauniya mai zaman kanta inda ta fara aikin tallafi a karkashinta a kananan hukumomin Yola ta arewa da ta kudu wadda sukafi kusa da ita.

Ta nan ne Binani ta sami daman tallafawa jama’a musamman ma iyalan da basuda galihu inda aka ga mata, matasa da masu larurar nakasa suka sami madogara tare da bata tallafin karatu wa marayu da sauran dalibai yan asalin jihan, gamida samar da motocin bada agajin gaggawa wa Musulmai da Kiristoci a kananan hukumomin.

Ire iren wadannan ayyukan ne ya janyo hankalin jama’a zuwa kanta wadda bayan mata fatan alheri suka kuma yi mata kira akan bukatar shiga siyasa domin ta samu daman tallafa musu sosai.
Inda batayi wata wata ba wurin turasu ga mai gidanta Dr. Modibbo wadda karara ya fito fili ya bayyana musu cewan matarsa batayi wannan aikin don a biyata ba kuma yaki yarda da bukatar tasu toh sai dai bayan matsa mishi lamba da jama’an sukayi daga karshe dai ya yarje mata da taje ta yiwa al’uma hidima.

Da farko dai jama’an turata sukayi zuwa majalisar wakilai inda ta wakilci kananan hukumomin Yola ta arewa Yola ta Kudu da Girei kuma mace ta farko data rike wannan matsayi, wadda bayan samu gamsasshen wakilci na gari daga gareta suka sake aikata zuwa majalisar dattawa.

Bayan aiwatar da aiki irin na madi ka ture a majalisar dattawan ne kuma jama’a suka sake ganin akwai bukatar su sake kiranta domin neman babbar kujeran shugabanci wadda hakan ne ya haifar da nasaran data samu a zaben fidda gwani na gwamna a jam’iyar APC inda ta kada abokan karawarta maza biyar wadda kuri’un da dukansu suka samu bai kai nata ba.

A bayyane yake cewa Binani bata taba neman wani kujeran siyasa don rajin kanta ba, a kulli yaumin jama’a ke mata kira shi yasa ta dabi’antu da dabi’an nan na cin zabe da gagarumin rinjaye saboda jama’an ne ke bukatarta ba akasin haka ba.

Babban dalilin da yasa jama’a suka yi mata kira data zo ta nemi kujeran gwamna shine yin la’akari da irin aikin kawo ci gaban kasa da tayi a majalisar dattawa. Duk da cewa ita sanata ce amma tana aiki tamkar wata gwamna inda akaga ta gina hanyoyi, asibitoci tona bohula, bada kayan tallafi wa dubbannin jama’a uwa uba shine kirkiro da dokoki wadda zai taimaki jama’an kasa baki daya.

A matsayinta na sanata ta mayar da Adamawa baki daya zuwa mazabarta inda jama’a daga Madagali zuwa Toungo zuwa Belel suka amfana da tallafin nata ta fannin koyon sana’o’i da dai sauransu wadda hakan ya taimaki iyalai da dama.

Wasu da dama na tunanin Binani tayi nasaran lashe zaben fidda gwani na gwamna ne saboda goyon bayan data samu daga mata, toh sai dai lamarin ba haka yake ba domin kuwa Binani tayi nasara ne saboda itace yar takara da tafi chanchanta da dacewa wacce ta samu goyon bayan maza da mata wadanda sukayi amannar cewa lokaci yagi da zasu biyata da irin tallafawa da take musu.

Tarihin nasararta zai sake maimaita kansa a zaben gomna dana yan majalisa dake tafe fiye ma dana zaben fidda gwani saboda yadda jama’a zasu fito kwansu da kwarkwatansu domin kada mata dimbin kuri’u sanadiyar kyawawan halayyarta na tausayi da tausayawa, a cewar Barata.

Toh sai dai a wani mataki na neman yabawa irin ta siyasa gomna Fintiri yayi wani yunkuri dake kama da kwafe irin ayyukan sanata Binani wadda nashi yafi kama da sayan kuri’u bayan dage zaben gomna dana yan majalisar jaha na ranar 11 ga watan maris da akayi.

A ranar talatan nan ne rahotanni suka nuna cewan gomnan ya rabawa mata 10,000 Naira dubu Hamsin Hamsin wadda hakan yasa masu fashin baki akan siyasa a jahar Adamawa suka soki lamirin gomnan bisa yadda ya nuna kwadayin sake komawa kan kujera karara ta hanyar sayan imanin jama’a.

Inda sukayi kira ga wadanda suka ci gajiyar shirin dasu karbi rabonsu amma su zabi wadda suke bukata a ranar zabe.

Sun tuna ko a baya ma yadda rashin tallafawa jama’a da gomnan baya yi yasa daya daga cikin makusantansa Hon. Umar ya shawarci gomnan da ya maida hankali wurin tallafawa jama’a domin saukaka musu wahalhalu da suke fiskanta inda daya daga cikin hadiman gomnan Sa’idu Sarki Zana yayi mishi barazana tare da shafa mishi kashin kaji saboda fadawa gomnan gaskiya da yayi inda ya tilastawa Umar janye kalamansa bisa dalilin rashin jin dadin kalaman da gomnan yayi.

Majiya daga gidan gomnatin ya tabbatar da cewa bayan dage zabe da INEC tayi daga ranar 11 ga watan maris zuwa 18 shine gomnan ya shirya wannan yaudaran da ya kira da sunan tallafi wa mata 10,000 toh sai dai bincike ya nuna cewa matan da sukaci gajiyar tallafin basu wuce 600 ba.

A bayyane yake cewa gomnan bai shirya aiwatar da wannan aikin tallafin ba amma da yake tallafin da sanata Binani keyi yana hanashi bacci, sai yayi amfani da dage zabe da akayi a matsayin wata kofa daya samu domin yaudaran iyayenmu mata ta hanyar yin karyan cewa zai tallafa musu da jarin 50,000.

A mahanga irin ta lissafi aikin tallafin baida wani tasiri kawai an shirya shi ne don yaudaran jama’a duba da yadda gomnatin bata da daman hada sunayen mata dubu goma a dan kankanin lokaci shi yasa aka gaggauta daukan sunayen matan wasu manya da yan uwansu, a cewar wani makusancin gomnatin.

Wani abu daya bayyana a matsayin tsoron guguwan sanata Binani da gomnan keji shine dakatar da ayyukan kungiyoyi masu zaman kansu bisa zargin za’a iya amfani dasu wurin sayan kuri’u, matakin, wadda dama anyi tsammanin daukansa yasa masu ruwa da tsaki a al’amuran yau da kullum bayyana cewan take hakkin jama’a ne da karfin gomnati.

Rahotanni sun kara bayyana cewan kokarin gomnan na dakatar da Binani shiga zabe ya gamu da cikas bisa yadda fannin shari’a tasa kafa ta shure bukatar gomnan.

Binani ta sami daman watayawa a fagen siyasan Adamawa ne sanadiyar fatan alheri da fatan nasara da jama’a ke mata bisa kyawawan dabi’unta.

Ta kasance mace ce mai karfin fafutukar nemowa jama’ar jaharta ayyukan ci gaba dana more rayuwa gamida samar da ingantattun dokoki wadda zasu kai kasan gaba.

An kiyasta cewan Binani ta tallafawa akalla mutum dubu dari wadda yayi sanadiyar cire yankuna da dama daga cikin kangin talauci kuma a shekaru hudu na baya bayan nan Binani a matsayinta na sanata tayi aiyukan ci gaba da gomna ne kadai zaiyi yunkurin aiwatarwa wadda ya taba rayukan al’uman Adamawa baki daya kuma hakan na daga cikin dalilan da yasa zataci zabe a Adamawa cikin ruwan sanyi, a cewar Barata.

Continue Reading

BABBAN LABARI

Copyright © 2020 VOA voiceofarewa.ng