Connect with us

DAGA JIHOHI

Zanga-zangar SARS: Shugaba Buhari ya gana da tsoffin shugabannin Najeriya

Published

on

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya yi wani taro ta intanet da dukkan tsofaffin shugabanin kasar a jiya Juma’a.

Shugabannin sun hada da Cif Olusegun Obasanjo da Janar Yakubu Gowon da Janar Ibrahim Badamasi Babangida da Cif Ernest Shonekan da kuma Goodluck Ebele Jonathan.

Shugabannin sun tattauna halin da kasar ke ciki, sakamakon zanga-zangar kyamar rundunar yan sandan SARS, wadda ta rikide zuwa rikici.

Mai ba da shawara na musamman ga shugaba Muhammadu Buhari kan yada labarai, Malan Garba Shehu ya ce tsohon shugaba Yakubu Gowon da kuma shugaban mai ci ne su ka yanke shawarar kiran taron shugabannin don nemo hanyoyin warware matsalolin da a ke ciki a kasar.

A cewar Garba Shehu tsofaffin shugabannin ‘sun ce sun gamsu da irin muhimman kalaman da ya yi a cikin jawabin nasa, musamman da ya amince cewa zanga zangar lumana abu ne da kundin tsarin mulki ya aminta a yi.’

‘Kuma sun gamsu cewa gwamnati ta amince da bukatun masu zanga zangar lumana kuma an fara aiki kan su.’

To amma Malan Garba Shehu ya ce ‘tsoffin shugabannin sun yi allah-wadai da kwace wannan tarzoma da yan ta’adda su ka yi.

‘Kuma fitinannun mutane suka zo suna kone-kone, suna sata, suna sakin yan fursuna da sauran irin wadannan abubuwa.’

Mai ba wa shugaban Najeriyar shawara ya kara da cewa taron ya tattauna asarar rayuka da dukiyoyi da a ka tabka sanadiyyar rikicin.

A cewarsa an kona gidaje da shaguna 205 kuma mutun 51 sun rasa rayukan su da su ka hada da jami’an tsaro 18.

Dangane da batun kisan masu zangza zangar a jihar Legas, Garba Shehu ya ce ‘ita gwamnatin Legas ta ce za ta daukin nauyin bincike kan abinda ya faru kuma kawo yanzu ba ta kawo cikakken bayanin abun da ya faru a can ba.’

‘Amma su sojoji sun nuna cewa ba ma su je wurin ba ballantana a ce sun yi harbi.’

DAGA JIHOHI

ƘUNGIYAR AYCMF TA GUDANAR DA TARUKA A JIHOHI SHIDA 22/5/2022

Published

on

KUNGIYAR MATASAN AREWACIN NIGERIA “AREWA YOUTHS CONCERN MEDIA FORUM” (AYCMF) TA GUDANAR DA TARUKA A JIHOHI SHIDA 22/5/2022.

 

Daga Kungiyar: Matasan Arewacin Nigeria “Arewa Youths Concern Media Forum” (AYCMF)

 

Tarukan sun gudana a jihohin Bauchi Borno Kaduna Gombe Kano Sokoto. anyi taron ne domin wayar wa yan uwa matasa kai dangane da halin da Arewa da al’ummar Arewa suke ciki da kokarin nunawa matasan mu muhimmancin hadin kai domin magance wasu daga cikin matsalolin matasan na arewa.

 

Taron ya maida hankali wajen kokarin nunawa matasa muhimmancin hadin kai a tsakanin mu domin tunkarar matsalolin yankin mu da dukkan karfin mu mussamman abunda yake ci mana tuwo a kwarya wato ta’addanci. kungiyar AYCMF ta tattauna sosai akan hanyoyin da za abi a dakile tunanin ta’addanci a kwakwalen matasan mu masu tasowa.

 

Kungiyar AYCMF tana fafutukar hada kan matasan Arewa a jihohi 19 da Abuja 20 domin mu zama tsintsiya madaurinki daya. masu magana da murya daya. karkashin inuwar Kungiyar domin cimma kyawawan manufofin ta guda biyar (5) da take aiki akai.

 

Kungiyar AYCMF tana maraba da dukkan wani matashi Namiji ko Mace mai kishin Arewa da al’ummar Arewa. kuzo mu hada kai domin samar da cigaban matasan mu a cikin kasar mu Nigeria. ayyukan kungiyar AYCMF yana fantsama lungu da sakon Arewacin Nigeria muna bukatar karin dakaru domin tabbatar da kyawawan manufofin kungiyar.

 

Kofar wannan kungiya abude take ga dukkan wani matashi mai kishin Arewa da al’ummar Arewa. kuzo mu hada kai domin dawo da martabar yankin mu da al’ummar mu a idon duniya.

 

Allah ya zaunar da Arewa lfy ya hada kawunan mu. mu zama tsintsiya madaurinki daya.

Sign:

AYCMF MANAGEMENT

22/5/2022

Continue Reading

DAGA JIHOHI

EFCC Na Zargin Tsohon Gwamnan Kano

Published

on

Daga Mujahid Wada Musa Kano

hukumar da ta ke yaki da hana cin hanci da rashawa EFCC ta garkame wani kango da kuma asibitin da ke jikinsa a unguwar Bompai ,mallakin tsohon gwamnan jahar Dr. Rabiu Musa Kwankwaso.

Tsohon gwamnan yana fuskantar zargi ne daga wasu ƴan fansho inda suka shigar da kararsa a shekarar 2015.
Asibitin da hukumar ta EFCC ta garkame din shi ne wanda ya bawa gwamnatin jahar Kano a lokacin da cutar corona ta fara kamari akasarnan dan killace masu fama da ita amma gwamnatin Kanon bata karba ba.

Sai dai wasu rahotanni mai kwanan watan 27 ga watan mayu na 2015 kwankwaso ya karbi gudunmawar naira miliyan 70-saba’in daga kananan hukumomi 44 na jahar Kano da jumullar kudi ya kai sama da biliyan 3 dan yakin neman zabensa na takarar shugaban kasa a 2015.

Continue Reading

DAGA JIHOHI

Ƴan bindiga sun hallaka ‘sama da mutum 35’ a jahar Zamfara

Published

on

By

Rahotanni daga jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya na cewa ‘yan bindiga sun kashe sama da mutum 40 a jerin hare-hare da suka kai a wasu kauyukan jihar.

Sai dai rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da kai harin, amma ta shaida wa BBC Hausa cewa mutum 35 aka kashe.

Lamarin ya faru ne a ƙauyuka fiye da biyar da ke karamar hukumar Maradun da ranar Alhamis sai dai bayanai ba su fito ba sai Juma’a.

Ganau sun shaida wa BBC cewa maharan sun je ƙauyukan Gidan Adamu da Gidan Maidaji da Bauci da Wari da Kyara da Gidan Maidawa kan babura sannan suka buɗe wuta.

Lamarin ya yi sanadin mutuwar mutum 42, a cewar wani mutum da muka tattauna da shi.

“Wannan lamari ya faru ne a jiya Alhamis tun daga karfe 12 na rana har zuwa bayan la’asar, a lokacin da ‘yan bindigar suka shiga shiyyar kan babura sama da 100,” in ji wani da ya shaida lamarin.

Wannan hari na zuwa ne kwana biyu kacal bayan da ƴn bindiga suka kashe mutum 18 a jihar Katsina.

Sannan kuma waɗannan hare-hare duk sun faru ne a yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da ƙoƙarin cetofiye da ɗalibai 100 da aka sace a wata makarantar kwana a jihar Kaduna.

Satar ɗaliban ita ce ta baya-baya cikin lamari irin sa da yake neman zama ruwan dare a arewacin Najeriya.

Continue Reading

BABBAN LABARI

Copyright © 2020 VOA voiceofarewa.ng